
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a zaben 2027, Atiku Abubakar, ya yi ikirarin cewa yana da hujjar da ke nuna cewa Shugaba Bola Tinubu ya kai shekaru 90, yana mai cewa zai iya gabatar da ita a gaban kotu idan bukatar hakan ta taso.
Atiku ya bayyana hakan ne a wata hira da BBC da aka wallafa ranar Juma’a, inda ya kuma kare kudirinsa na sake neman kujerar shugaban kasa.
Ya ce yana da ‘yancin yin takara bisa kundin tsarin mulki, tare da bayyana kwarewarsa da kishin kasa a matsayin wasu daga cikin dalilan da suka sa yake son ci gaba da neman shugabancin Najeriya.
Atiku ya ce, “Kuna da Shugaban kasa mai shekaru 90 a yanzu kuma marar lafiya, yayin da ni nake cikin koshin lafiya da karfi. Don haka me ya sa ba zan gabatar da kaina domin yi wa kasata hidima ba?
“Kun je kun zabi wanda yake da shekaru 90. Ina da hujjar cewa Shugaba Tinubu yana da shekaru 90, kuma zan gabatar da ita a gaban kotu.”
Ya kuma alakanta matsalar rashin tsaro a Najeriya da gazawar gwamnati, musamman a bangaren tsaro da ‘yan sanda, yana mai alkawarin magance matsalar cikin shekara guda idan aka zabe shi.