
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya ce ba zai janye ƙudurinsa na dawo da tallafin man fetur ba idan ya samu nasara a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Atiku, wanda shi ne ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, ya ce manufarsa ita ce rage tsadar rayuwa da sauƙaƙa wa ’yan Najeriya wahalhalun da cire tallafin man fetur ya haifar.
Ya ce tsarin da yake shirin amfani da shi zai mayar da hankali kan tallafa wa matatun man fetur na cikin gida da rage tsadar samar da mai. Haka kuma, za a ƙayyade adadin kuɗin tallafin tare da ware su cikin kasafin kuɗi, sannan masu zaman kansu su riƙa binciken yadda ake kashe kuɗin.
A wata sanarwa da babban mataimakinsa kan harkokin sadarwa, Phrank Shaibu, ya fitar, ya ce kalaman wani mataimakin Atiku na cewa “Atiku zai dawo da tallafin man fetur sannan ya cire shi daga baya” ba su yi daidai da aniyar ɗan takarar ba.
Shaibu ya ce, “Babbar manufar ita ce rage tsadar rayuwa da mayar wa ’yan Najeriya ƙarfin saye.”
Ya ƙara da cewa Atiku zai mayar da hankali wajen rage tsadar samar da kayayyaki da sufuri, tare da ƙara samar da man fetur a cikin gida.