
Hukumar Babban Birnin Tarayya (FCTA) ta ci gaba da rushe gidaje da wasu gine-gine da aka gina a kan hanyoyin ruwa da wuraren da zaizayar ƙasa ke shafar su a Abuja.
Matakin ya biyo bayan ambaliyar ruwa da ta afku a ranar 16 ga Agusta, inda aka samu cunkoson ababen hawa tare da nutsewar wasu motoci a yankunan Maitama, Wuse 2, Gudu, Lokogoma da wasu sassan babban birnin tarayya.
Bayan ambaliyar, Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya bayar da umarnin a fara rushe gine-ginen da ke toshe hanyoyin ruwa a Maitama da sauran wuraren da ambaliyar ruwa ke yawan shafa.
Wike ya bayar da umarnin ne bayan ya duba wuraren da ambaliyar ta shafa, inda ya ce rushewar za ta ci gaba ba tare da la’akari da harkokin siyasa ko matsayin masu gine-ginen ba.
A ranar Talatar da ta gabata, FCTA ta fara rushe gine-gine da aka gina a kan hanyoyin ruwa a kusa da Maitama. Sai dai rahoton TheCable ya nuna cewa wasu daga cikin gine-ginen da aka riga aka rushe an fara sake ginawa.
A yankin Wuye kuma, jami’an FCTA sun gudanar da aikin tabbatar da bin ƙa’ida, inda suka rushe gidaje, katanga da wasu gine-gine da aka gano suna kan hanyoyin ruwa.