Matawalle Ya Ce Zai Tattara Wa Tinubu Ƙuri’u Miliyan 20 A 2027



Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya bayyana cewa yana da burin tara wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ƙuri’u miliyan 20 a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Matawalle ya bayyana hakan ne ranar Talata a Abuja, yayin da magoya bayansa da wasu ’yan jam’iyyar APC suka tarbe shi bayan dawowarsa Najeriya.

Ya ce zai fara tattara bayanai da neman ƙuri’u a faɗin jihohin Najeriya 36 da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja.

Matawalle ya ce, “Kamar yadda kuka sani, an fara kamfen, kuma burina shi ne in kawo wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ƙuri’u miliyan 20 a zaɓen shugaban ƙasa na 2027… Kuma a shirye nake in yi duk abin da zan iya domin tabbatar da mun cimma wannan buri.”

Ya ce akwai dalilai da dama da suka sa yake ganin ya kamata a sake zaɓar Tinubu a 2027, ciki har da abin da ya bayyana a matsayin ƙoƙarin shugaban wajen inganta ayyukan yi ga matasa, tsaro da tattalin arzikin ƙasa a cikin shekaru ukun da ya yi yana mulki.

Rahotanni sun nuna cewa Matawalle na cikin jami’an da aka bai wa muƙami a kwamitin yaƙin neman zaɓen APC na 2027.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...