Iran Ta Zartar Da Hukuncin Kisa Kan Sama Da Mutane 500 A 2026

Muhammadu SabiuHausa50 minutes ago



Wata ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Iran Human Rights (IHR), mai hedikwata a Norway, ta ce Iran ta zartar da hukuncin kisa kan aƙalla mutane 511 tun farkon shekarar 2026.

Ƙungiyar ta ce daga cikin waɗanda aka kashe akwai aƙalla mutane 29 da ake zargin suna da alaƙa da zanga-zangar adawa da gwamnati da aka gudanar a watan Janairu.

Daraktan IHR, Mahmood Amiry-Moghaddam, ya ce hankalin duniya kan rikicin da ke tsakanin Amurka da Iran da kuma sake buɗe Mashigar Hormuz ya bai wa gwamnatin Iran damar ci gaba da aiwatar da hukuncin kisa.

Ya ce, “Yayin da hankalin duniya ya karkata ga rikicin da ke tsakanin Amurka da Iran da kuma sake buɗe Mashigar Hormuz, hakan ya bai wa gwamnatin Iran ƙarin damar ci gaba da zartar da hukuncin kisa.”

IHR ta ƙara da cewa aƙalla mata 16 na cikin mutanen da aka zartar wa hukuncin kisan, yayin da wasu daga cikin waɗanda aka kashe ke da alaƙa da ƙungiyoyin adawa da gwamnatin da aka haramta.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...