
Jaridar Wall Street Journal ta ruwaito cewa wasu manyan jami’an leƙen asiri da na soja sun gargadi Shugaban Amurka, Donald Trump, game da illolin fara yaƙi da Iran, amma ya yi watsi da gargadin.
Rahoton ya bayyana cewa Trump ya ƙaddamar da hare-haren ne bisa ra’ayin cewa Iran na cikin wani yanayi na rauni fiye da kowane lokaci cikin shekaru da dama.
Jaridar ta ce Tulsi Gabbard, wadda a lokacin ita ce Daraktar Hukumar Leƙen Asiri ta Ƙasa ta Amurka, ta gargadi Trump kwanaki kaɗan kafin hare-haren ranar 28 ga Fabrairu cewa kashe shugaban Iran na iya haifar da kafa gwamnati mai tsattsauran ra’ayi.
Gabbard ta yi gargadin cewa sabuwar gwamnatin za ta iya ƙara himma wajen ƙera makaman nukiliya.
Rahotannin wasu kafafen yaɗa labaran Amurka sun kuma mayar da hankali kan asarorin yaƙin da ba a bayyana a fili ba, da sauyin dabarun Washington daga hare-haren soja zuwa matsin tattalin arziki.
Haka kuma, ana nuna damuwa kan tasirin rikicin ga Jam’iyyar Republican a zaɓukan tsakiyar wa’adi da kuma ƙarin rashin tsaro a cikin Amurka.