Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane, Sun Kuma Ƙona Wani Ƙauye A Zamfara



Wasu ’yan bindiga sun kai hare-hare kan al’ummomin Bardoki da Bunkasau da ke ƙananan hukumomin Gummi da Bukkuyum a Jihar Zamfara, inda suka kashe mutane da dama tare da jikkata wasu.

Rahoton da wani mai sharhi kan harkokin tsaro, Bakatsine, ya wallafa a shafinsa na X ya ce maharan sun lalata gidaje da dukiyoyi, lamarin da ya tilasta wa mazauna yankunan tserewa domin tsira.

Bakatsine ya ce, “A wannan rana da rana, ’yan bindiga sun kai hari Bardoki da ke ƙaramar hukumar Gummi da Bunkasau da ke ƙaramar hukumar Bukkuyum a Jihar Zamfara. Hare-haren sun yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da jikkata wasu, yayin da aka lalata gidaje da dukiyoyi. Mazauna da dama sun tilastawa barin al’ummominsu domin neman tsira. Wasu ’yan Civilian JTF da suka nufi Bunkasau domin mayar da martani su ma sun fada cikin kwanton baunar ’yan bindigar.”

Ya ƙara da cewa bayan harin Bardoki, ’yan bindigar sun banka wa al’ummar Ruwan-Kura wuta, lamarin da ya sake tilasta mazauna garin guduwa.

“Bayan harin Bardoki, ’yan bindigar sun banka wa al’ummar Ruwan-Kura wuta, lamarin da ya tilasta wa mazauna tserewa. Wasu daga cikinsu yanzu suna samun mafaka a Daki Takwas, yayin da wasu suka nemi tsira a Dargaje. Waɗannan mutane ne da suka rasa gidajensu, ’yan uwansu da duk abin da suka gina,” in ji Bakatsine.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...