Tinubu Ya Amince Da Rage Kuɗin Sufuri A Faɗin Najeriya

Muhammadu SabiuHausa39 minutes ago



Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da kafa kwamitin haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin tarayya da jihohi domin aiwatar da matakan rage kuɗin sufuri a faɗin ƙasar.

Tinubu ya bayyana hakan bayan ganawarsa da ƙungiyar gwamnonin Najeriya, inda ya ce gwamnonin sun amince da rage kuɗin sufuri a jihohinsu, musamman ta hanyar amfani da motocin CNG da na lantarki.

Shugaban ya ce gwamnatin tarayya ta sauya motocin sama da 120,000 daga amfani da man fetur zuwa CNG, tare da shirin kammala wasu kayan sauya motocin sama da 100,000.

Ya kuma ce an bayar da umarnin samar da ƙarin tashoshin CNG 500, baya ga wasu 500 da aka riga aka amince da samarwa a farkon shekarar.

Tinubu ya ce gwamnati na fatan ’yan Najeriya za su fara amfana da matakan daga ranar 1 ga Oktoba.

“Muna fatan daga ranar 1 ga Oktoba, ’yan Najeriya su fara cin moriyar wannan tanadi ta hanyar samun sauƙin kuɗin sufuri,” in ji Tinubu.

Ya ƙara da cewa gwamnatin tarayya da jihohi sun amince da fara aiwatar da shirin nan take.

“Mun amince cewa idan man fetur ya yi arha, kuɗin sufuri ma ya kamata ya ragu,” in ji shi.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...