Jam’iyyun Adawa Sun Tsayar Da 31 Ga Agusta Don Haɗa Kai Wajen Kayar Da Tinubu

Muhammadu SabiuHausa30 minutes ago



Wasu manyan jam’iyyun adawa a Najeriya sun tsayar da ranar 31 ga Agusta, 2026, domin gudanar da taron da zai fara shirin haɗa kansu gabanin zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Wani jagoran jam’iyyun adawa, Salihu Lukman, ne ya bayyana hakan a madadin ƙungiyar G100. Ya ce manufar taron ita ce fara tattaunawa kan tsarin, ƙa’idoji da hukumomin da jam’iyyun za su yi amfani da su wajen haɗin gwiwa a zaɓen 2027.

Ya ce an cimma matakin ne bayan shafe makonni ana tattaunawa da shugabannin jam’iyyun ADC, APM, NDC, PDP, PRP da SDP.

Lukman ya ce tattaunawar ta haifar da wani tsari mai suna A Framework for Opposition Cooperation and Coordination, wanda ya bayyana wuraren da jam’iyyun za su iya haɗin gwiwa, tare da mutunta bambance-bambancen tarihinsu da manufofinsu.

Ya ce, “Haɗin gwiwa ba ya nufin kowace jam’iyya ta ɓace cikin wata. Tambayar farko da ke gaban shugabannin jam’iyyun ba ita ce wa zai jagoranci tikitin ba. Abin da ya kamata a fara tambaya shi ne, me za mu iya yi tare domin wannan ƙasa?”

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...