Trump Ya Ce Amurka Ba Ta Neman Tattaunawa Da Iran

Muhammadu SabiuHausa47 minutes ago



Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce gwamnatinsa ba ta neman ganawa ko tattaunawa da Iran a halin yanzu.

Trump ya bayyana hakan a fadar White House yayin da yake amsa tambayoyin ’yan jarida. Ya ce Amurka ba ta da wani abu mai yawa da za ta tattauna da Iran a yanzu.

Ya ce, “Ba mu da wani abu da yawa da za mu ce game da Iran yanzu. Ba ma son yin magana da su, kuma ba ma son ganawa ko yin shawarwari da su.”

Shugaban na Amurka ya kuma ce Mashigar Hormuz a buɗe take, yana mai cewa jiragen ruwa da dama na ci gaba da ratsa mashigar.

Trump ya ƙara da cewa ana fitar da miliyoyin ganga na mai ta Mashigar Hormuz a kullum, yayin da Amurka ke amfani da rundunar sararin samaniyarta, “Space Force”, wajen sa ido kan yankin Tekun Fasha da mashigar.

Ya kuma ce Amurka ta cire dukkan nakiyoyin da aka sanya a Mashigar Hormuz, duk da cewa a wasu lokuta ana jin harbe-harbe a yankin.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...