Trump Ya Yi Barazanar Kai Wa Oman Hari Kan Rikicin Hormuz



Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar kai wa Oman hare-haren bama-bamai masu tsanani idan ƙasar ta tsoma baki ko ta kawo cikas ga matakan Amurka a rikicin da take yi da Iran kan mashigar ruwan Hormuz.

Trump ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta wayar tarho da gidan talabijin na Fox News ranar Litinin.

Barazanar ta zo ne bayan Iran da Oman sun sanar da cimma matsaya kan hanyar da jiragen ruwa za su bi wajen ratsa mashigar Hormuz.

A halin da ake ciki, wani rahoto ya ce Amurka na da hanyar sadarwa kai tsaye da Rundunar Juyin Juya Halin Musulunci ta Iran (IRGC), sai dai rundunar ta musanta cewa tana tattaunawa da Amurka.

Jami’an Iran sun kuma ce suna dab da kammala yarjejeniya da Amurka kan yadda za a rika zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigar Hormuz, wanda ya kasance ɗaya daga cikin muhimman batutuwan da ake tattaunawa a kai.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...