Iran Ta Yi Alkawarin Bada Ladan $60,000 Ga Matar Da Ta Kama Sojan Amurka



Babban kwamandan sojojin Iran, Amir Hatami, ya sanar da cewa ƙasar za ta ba duk macen da ta kashe ko kama wani sojan Amurka tare da miƙa shi ga hukumomi ladan dala 60,000.

Hatami ya ce maza da suka aikata hakan za su samu ladan dala 30,000, wanda ya bayyana cewa ya yi daidai da kusan biliyan biyar na toman.

Ya bayyana hakan ne a wani taro na bikin Ranar ’Yan Jarida, inda ya kuma ce za a sayi makamin duk wanda ya kashe sojan Amurka da ninki biyu na kuɗinsa, sannan a ba shi sabon makami.

A cewarsa, za a ajiye makamin a wani gidan tarihi domin tunawa da irin waɗannan ayyuka.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...