2027: Atiku Ya Ce Bai Da Tabbacin INEC Za Ta Yi Abin Da Ya Dace

Muhammadu SabiuHausa12 minutes ago


Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a zaben 2027, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa ba shi da cikakken yakinin cewa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) za ta gudanar da zaben cikin adalci.

Atiku ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da BBC Hausa ranar Juma’a, inda ya zargi gwamnatin tarayya karkashin jam’iyyar APC da yin tasiri a kan hukumar zaben.

Ya ce, “Ba ni da yakinin cewa INEC za ta yi abin da ya dace saboda tana karkashin tasirin gwamnatin da ke mulki a yanzu.”

Atiku ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su fito da yawa domin kada kuri’a, tare da kare kuri’unsu har zuwa lokacin da za a kidaya su.

Ya ce, “Shi ya sa muke kira ga ‘yan Najeriya da su fito da yawa, su kada kuri’unsu, su kare kuri’unsu, kuma su tabbatar da cewa kuri’unsu sun kirga.”

Da aka tambaye shi kan zargin cewa shi ne babban cikas ga hadakar G-100, Atiku ya yi watsi da zargin, yana mai cewa ba shi da tushe.

Ya ce, “Wannan zargin ba shi da tushe. Ni, Atiku Abubakar, ina cikin wadanda suka fara wannan hadaka, kuma da dama daga cikin wadanda suka fara wannan tafiya tare da ni har yanzu suna cikinta.”

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...