Kamfanin Uber Ya Sanar Da Ficewa Daga Najeriya Bayan Shekaru 12



Kamfanin safarar fasinjoji ta hanyar manhajar zamani, Uber, ya sanar da dakatar da ayyukansa a Najeriya daga ranar 2 ga Satumba, 2026, bayan shafe shekaru 12 yana aiki a kasar.

Kamfanin ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba, inda ya ce ya yanke shawarar ne bayan gudanar da cikakken nazari kan harkokin kasuwancinsa.

Uber ya ce, “Muna rubuto wannan ne domin sanar da ku wani labari mai matukar wahala. Bayan cikakken nazari kan harkokin kasuwancinmu, mun yanke shawarar dakatar da ayyukanmu a Najeriya daga ranar 2 ga Satumba, 2026.”

Kamfanin ya ce tun lokacin da ya fara aiki a Legas a shekarar 2014, ya dauki aiki a Najeriya a matsayin wata dama ta kasancewa cikin rayuwar jama’a ta yau da kullum tare da hada su da masu samar da harkokin sufuri masu zaman kansu.

Uber ya kara da cewa, “Ko tafiyar safe ce zuwa aiki, ziyartar masoya, ko zagayawa cikin birni, muna godiya da amincewar da kuka ba dandalinmu wajen hada ku da direban da zai kai ku inda kuke cikin aminci.”

Kamfanin ya kuma nemi afuwar kwastomominsa kan matsalar da matakin zai iya haifarwa, yana mai cewa, “Mun san wannan na iya kawo cikas ga tsarin rayuwarku na yau da kullum, kuma muna neman afuwar ku da gaske kan wannan rashin jin dadi.”

Uber ya ce cibiyar taimakonsa za ta ci gaba da aiki har zuwa ranar 23 ga Satumba, 2026, domin taimaka wa kwastomomi wajen magance tambayoyi ko matsalolin karshe da suka shafi asusunsu.

A karshe, kamfanin ya ce, “Muna godiya da yadda kuka karbe mu cikin garinku.”

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...