Atiku Ya Soki NELFUND, Ya Yi Alkawarin Yafe Basussukan Dalibai



Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya soki tsarin rancen karatu na NELFUND, yana mai cewa shirin ba tallafin karatu ba ne, sai dai bashi da dalibai za su biya daga baya.

Atiku, ta bakin mai magana da yawunsa kan harkokin yada labarai, Phrank Shaibu, ya ce idan aka zabe shi shugaban kasa a 2027, gwamnatinsa za ta rage kudaden ilimi tare da yafe basussukan daliban da suka cancanta bayan gudanar da cikakken nazari kan tsarin.

Ya ce, “Rance ba tallafin karatu ba ne; bashi ne da dalibi zai biya.”

Atiku ya kuma kalubalanci gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da ta bayyana alkaluman da ke nuna yadda shirin rage farashin man fetur da take aiwatarwa zai shafi ayyukan NELFUND, albashin ma’aikata da kuma mafi karancin albashi.

Ya ce ya kamata gwamnati ta samar da cikakken bayani kan yadda manufofinta na tattalin arziki za su shafi bangaren ilimi da walwalar ma’aikata.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...