Yan kungiyar IPMAN za su rage farashin mai a Abuja

Kungiyar IPMAN ta Dillalan Mai Masu Zaman Kansu ta ce gidajen mai dake faɗin birnin tarayya Abuja za su fara rage farashin man fetur nan da yan kwanaki masu zuwa.

Chinedu Ukadike sakataren yaɗa labaran ƙungiyar IPMAN shi ne ya bayyana haka lokacin da yake zantawa da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN a birnin tarayya Abuja.

Ukadike ya ce masu gidajen man sun shirya sake duba farashin nasu da kuma dabarar kasuwancinsu a yayin da sabon kaya ke shirin shiga kasuwa.

Zuwan sabon man zai haifar da sauyi a kasuwar ya kara da cewa yan kasuwar za su yi sauye-sauyen da su ka dace domin tabbatar da cewa masu amfani da shi sun cigaba da saya.

Mai magana da yawun na IPMAN ya ce basu da masaniyar ranar da za a samu man saboda a fada musu takamaiman ranar da za a fara kawo ba.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...