Ƴar Najeriya Ta Zama Shugabar Kwalejin Shari’a A Canada

Muhammadu SabiuHausa44 minutes ago


Wata ’yar asalin Najeriya, Dokta Ibironke Odumosu-Ayanu, an naɗa ta shugabar Kwalejin Shari’a ta Jami’ar Saskatchewan da ke Canada.

Jami’ar ta bayyana cewa Odumosu-Ayanu za ta fara wa’adin shekaru biyar daga ranar 1 ga Oktoba, 2026.

Kafin sabon naɗin, Odumosu-Ayanu tana matsayin mataimakiyar shugabar kwalejin mai kula da bincike da karatun digiri na gaba. Ta shiga aikin koyarwa a Kwalejin Shari’a ta Jami’ar Saskatchewan a shekarar 2008.

Jami’ar ta sanar da naɗin nata a ranar 1 ga Satumba, 2026, a cikin wata sanarwa da Patti McDougall, mataimakiyar shugaban jami’ar mai riƙon ƙwarya, ta fitar.

McDougall ta yaba da ƙwarewar Odumosu-Ayanu a fannin ilimi da kuma kwarewarta wajen jagoranci.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...