Miliyoyin ’Yan Najeriya Na Cikin Talauci — Makinde

Muhammadu SabiuHausa17 minutes ago



Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ya bayyana cewa miliyoyin ’yan Najeriya na ci gaba da rayuwa cikin talauci duk da irin ƙoƙarin da suke yi wajen inganta rayuwarsu.

Makinde ya bayyana hakan ne a cikin wasiƙarsa, inda ya ce matsalolin Najeriya sun fi ƙarfin a danganta su da mutanen da ke riƙe da mukaman gwamnati kawai.

Ya ce duk da sauye-sauyen gwamnatoci da manufofin da aka gabatar a tsawon shekaru, har yanzu ’yan Najeriya da dama ba sa samun ingantaccen sauyi a rayuwarsu.

Gwamnan ya kuma ce matasa da dama ba sa ganin wata hanya bayyananniya da za ta kai su daga makaranta zuwa samun kyakkyawar dama a rayuwa.

Ya ce matsalar rashin tsaro ma na ci gaba da jefa ’yan Najeriya cikin wahala, yayin da wasu hukumomin da aka kafa domin taimaka musu ba sa gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Makinde ya ce wannan yanayi na nuna cewa matsalar Najeriya ta fi ta mutanen da ke kan mukaman gwamnati a kowane lokaci.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...