
Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Radda, ya tabbatar wa Shugaba Bola Tinubu cewa jihar za ta mara masa baya a ƙoƙarinsa na sake lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Radda ya bayyana hakan ne a ranar Asabar a Katsina yayin ƙaddamar da tsarin PBAT Door-to-Door Movement, wata ƙungiya da ke tattara goyon bayan jama’a tun daga matakin ƙasa domin Tinubu.
Gwamnan ya ce Katsina jiha ce mai ƙarfi ga jam’iyyar All Progressives Congress (APC), wadda yake cewa tana da haɗin kai a dukkan ƙananan hukumomi 34 na jihar.
Ya kuma yabawa manufofin tattalin arzikin gwamnatin Tinubu, yana cewa garambawul ɗin da shugaban ya kawo ya taimaka wajen ƙara wa gwamnatocin jihohi kuɗaɗen gudanar da ayyuka tare da ƙarfafa ’yancin kuɗaɗen ƙananan hukumomi.
A nasa jawabin, Kestin Ebimorbowei Pondi, wanda ya wakilci wanda ya kafa ƙungiyar, High Chief Government Oweizide Ekpemupolo, wanda aka fi sani da Tompolo, ya buƙaci mambobin ƙungiyar su kai kamfen ɗin zuwa unguwanni, al’ummomi, kasuwanni da gidaje.
Shugaban APC na Katsina, Dr Bishir Gambo Saulawa, ya bayyana jam’iyyar a matsayin iyali guda mai haɗin kai, tare da yin kira da a haɗa kai tsakanin ƙungiyar da tsarin APC na jihar.
An kuma rabawa masu kula da ƙungiyar a ƙananan hukumomi 34 motocin kamfen domin gudanar da ayyukansu.