
Shugaban kungiyar Fulani makiyaya ta Miyetti Allah Cattle Breeders Assembly of Nigeria(MACBAN) a jihar Benue, Ardo Risku Muhammad ya rasu.
An kashe Muhammad ne tare da wani makusancinsa da ake kira Yakubu Isa a wani harin kwantok ɓauna da aka kai musu a Okwudu dake ƙaramar hukumar Otukpo ta jihar Benue.
Babban ɗan marigayin, Muhammad Idris wanda ya tabbatarwa jaridar Daily Trust faruwar lamarin ya ce mutane biyun da aka kashe na kan hanyarsu ne ta dawowa daga wani zaman taron sulhu da aka yi a karamar hukumar Ohimini lokacin da aka kai musu farmaki da ƙarfe 02:00 na rana.
Idris ya ce DPO din yan sanda na karamar hukumar Ohimini ne ya kira taron sulhu inda mahaifin nasa ya halarta tare da Isa kafin daga bisani a kai masa harin da ya yi ajalinsa.
Ya yi zargin cewa maharan da su ka yiwa mahaifin nasa kwanton bauna suka harbe shi take a wurin.
Shugaban karamar hukumar Ohimini, Gabriel Adole ya faɗawa jaridar ta Daily Trust cewa an kira taron sulhu ne bayan da wasu manoma su ka yi korafin bullar fulani makiyaya a yankin.
Ya ce taron sulhun ya haifar da ɗa mai ido kuma marigayin ya bar wurin taron lafiya amma abun ta kai ci aka kashe shi a Otukpo.

