Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kwara, Victor Olaiya, ya bayar da umarnin gudanar da sahihin bincike kan mutuwar wasu ‘yan’uwa guda uku da suka mutu a cikin mota da ke tsaye a garin Ilorin babban birnin jihar.
Lamarin dai ya faru ne a ranar Lahadi da ta gabata.
A cewar wani mazaunin unguwar, ’yan sandan sun kasa shiga ginin saboda kofar a kulle da kwaɗo take, kuma babu kowa a gidan.
Rahotanni sun nuna cewa daga bisani ‘yan sandan sun zarce zuwa gidan mahaifiyar marigayiyar da ke kan titin Taiwo Isale, Ilorin, inda take ta jimami bayan ta suma sakamakon mutuwar ‘ya’yanta a ranar Lahadi.
Ƴan sandan sun tambayi uwar a kan me ya sa ba ta kai rahoton lamarin a hukumance gare su ba.