Yunwa da ƙishirwa na yi wa ƙananan yara barazana a Gaza

A yayin da Isra’ila ke ci gaba da kai munanan hare-hare a Gaza, ƙananan yara na cikin wadanda abin ya fi shafa.

Baya ga haka rashin ruwan sha da abinci na ci gaba da yin barazana.

“Abin da muke gani a Gaza a yanzu shi ne kisan gillar da ake yi wa kananan yara a hankali,” in ji Alexandra Saieh, shugabar manufofin agaji da bayar da shawarwari a kungiyar Save the Children International.

Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta ce yara shida ne suka mutu a arewacin Gaza sakamakon rashin ruwa da rashin abinci mai gina jiki a asibitocin Kamal Adwan da al-Shifa, yayin da wasu ke cikin mawuyacin hali.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]