Yunwa da ƙishirwa na yi wa ƙananan yara barazana a Gaza

A yayin da Isra’ila ke ci gaba da kai munanan hare-hare a Gaza, ƙananan yara na cikin wadanda abin ya fi shafa.

Baya ga haka rashin ruwan sha da abinci na ci gaba da yin barazana.

“Abin da muke gani a Gaza a yanzu shi ne kisan gillar da ake yi wa kananan yara a hankali,” in ji Alexandra Saieh, shugabar manufofin agaji da bayar da shawarwari a kungiyar Save the Children International.

Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta ce yara shida ne suka mutu a arewacin Gaza sakamakon rashin ruwa da rashin abinci mai gina jiki a asibitocin Kamal Adwan da al-Shifa, yayin da wasu ke cikin mawuyacin hali.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...