Ƴan bindiga sun kashe mutane 12 da jikkata biyu a jihar Adamawa 

Sulaiman SaadArewa22 minutes ago

‘Yan bindiga sun kashe mutane goma sha biyu da safiyar Litinin a kauyen Nzangula, unguwar Guyaku, dake karamar hukumar Gombi ta jihar Adamawa. 

Shugaban karamar hukumar Gombi, Mista Markus Ishaya, ya bayyana hakan a cikin wata hira ta musamman da  ya yi da jaridar PUNCH Online a ranar Litinin. 

A cewar Ishaya, harin ya faru ne a unguwar Guyaku, inda rahoto daga kauyen Nzangula ya nuna cewa mutane 12 aka kashe, yayin da wasu biyu suka jikkata kuma suna karɓar magani a Asibitin Cottage da ke Gombi. 

Ishaya ya ƙara da cewa an yi garkuwa da wata mata, yayin da aka ƙone cocin EYN, gidaje uku da kuma lalata shaguna biyu. 

Ya ce “Rahoto daga kauyen Nzangula na unguwar Guyaku, Gombi LGA, ya nuna cewa mutane 12 aka kashe, biyu sun jikkata kuma suna asibitin Cottage, Gombi. 
“An yi garkuwa da wata mata. An ƙone cocin EYN. Gidaje uku aka ƙone, kuma shaguna biyu aka lalata.” 

Kusan makonni biyu bayan ‘yan ta’adda sun kashe fiye da mutane goma a karamar hukumar Hong ta jihar Adamawa, an sake ruwaito cewa mutane 11 aka kashe a ranar Litinin a kauyen Zaranga da ke karamar hukumar Gombi

Wani mazaunin kauyen, wanda ya yi magana a kan sharadin za a aboye sunansa, ya ce Boko Haram sun mamaye kauyen da safiyar Litinin, suna harbi da ƙona gidaje. 

Ya ce: “A halin yanzu, an samo gawarwaki 11. Mutane da dama har yanzu ba a gansu ba. Tawagar bincike da jami’an tsaro suna cikin daji suna neman mutanen da suka ɓace.” 

Wani mazaunin kauyen ya ce matarsa da wasu ‘yan uwansa biyu suna cikin gawarwakin da aka samo. 

Ya ce: “Matata da wasu ‘yan uwana biyu suma sun mutu a lokacin mamayar safiyar da aka yi wa kauyena.” 

Har yanzu hukumomi ba su fitar da wata sanarwa ta hukuma game da harin ba. 


Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...