Jam’iyun APC da PDP sun shigar da ƙara kan zaɓen gwamnan Osun

Sulaiman SaadArewaHausa32 minutes ago

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da Peoples Democratic Party (PDP) sun shigar da ƙorafe-ƙorafe daban-daban kan sake zaɓen Ademola Adeleke a matsayin gwamnan jihar Osun. 

An nuna ƙorafe-ƙorafen a kan allon sanarwa na ofishin kotun sauraron ƙarar zaɓen gwamna dake Osogbo a ranar Litinin, wanda hakan ya nuna  fara aiwatar da shari’ar da ke kalubalantar sakamakon zaɓen gwamna da aka gudanar a ranar 15 ga Agusta. 

A cewar Pefe Belemore, sakataren kotun, an tabbatar da shigar da ƙorafe-ƙorafen. 

Ƙorafin APC, mai lamba EPT/OS/GOV/01/2026, an shigar da shi ta hannun ɗan takarar jam’iyyar, Munirudeen Bola Oyebamiji, kan Adeleke, jam’iyyar Accord da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC). 

Ƙorafin PDP kuma, mai lamba EPT/OS/GOV/02/2026, Adebayo Olugbenga Adedamola ne ya shigar da shi kan Adeleke, INEC da Accord. 

Nuna waɗannan ƙorafe-ƙorafen zai ba da damar a aika da takardun shari’a ga ɓangarorin da abin ya shafa sannan a ci gaba da sauraron shari’a a gaban kotun. 

Adeleke, ɗan takarar jam’iyyar Accord, an ayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara bayan ya samu ƙuri’u 511,067 a zaɓen ranar 15 ga Agusta. 

Shigar da ƙorafin APC ya zo ne kwanaki kaɗan bayan Oyebamiji ya ce ya amince da sakamakon zaɓen tare da taya Adeleke murna. 

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar 29 ga Agusta, Oyebamiji ya ce ya amince da sakamakon zaɓen, sai dai ya nuna damuwa kan tashin hankali da aka samu a lokacin zaɓen. 

Ya ce: “Duk da mun amince da sakamakon zaɓen kuma mun taya wanda ya yi nasara murna, ba za mu manta da mummunan tashin hankalin da ya faru da rayukan da aka rasa ba.” 

Ya ƙara da cewa tawagarsa za ta ci gaba da neman “adalci da gaskiya ta hanyar doka da kundin tsarin mulki” idan akwai sahihan damuwa. 

Adeleke ya kira Oyebamiji da sauran ‘yan takara da su ajiye bambance-bambancen siyasa su goyi bayan gwamnatinsa bayan sake zaɓensa. 

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...