

Amurka ta kawowa Rundunar Sojan Sama ta Najeriya kayan aikin soja da aka sauke su a Lagos da Kainji dake jihar Neja.
Rundunar sojan Amurka da ake kira da Africom (US Africa Command) wacce ke lura da Nahiyar Afrika ce ta bayyana haka wani sako da ta wallafa shafinta na yanar gizo a ranar Alhamis inda ta ce an kawo kayan aikin ne a watan Satumba ta hanyar jirgin saman sojan Amurka kirar C-17.
Rundunar ta ce “kawo kayan aikin wani bangare ne na yarjejeniyar sayen kayan soja tsakanin Amurka da Najeriya.”
“Kawo kayan aikin yana kara karfafa dangantakar dabarun soja tsakanin kasashen biyu domin tallafawa kokarin Najeriya na yaki da ta’addanci a yankin,” a cewar Africom
A watan da ya gabata, kwamandan Africom, Dagvin Anderson, ya bayyana cewa Amurka ta janye yawancin sojojinta daga Najeriya bayan aikin da aka yi a watan Mayu wanda ya kashe Abu-Bilal al-Minuki, mataimakin shugaba na ISIS, a Tafkin Chadi.