
Rundunar Sojin Najeriya ta Operation FANSAN YAMMA ta kama mutane 3 da ake zargi mambobin wata kungiyar ’yan ta’adda ne a wasu samamen da aka gudanar a sassan Jihar Kaduna.
Wadanda aka kama sun hada da wani da ake zargi da jagorantar kungiyar, wata mata da ake zargi da safarar harsasai da kuma wani da ake zargi da samar da kayan aiki ga ’yan ta’addan.
An gudanar da ayyukan ne ranar Laraba a kananan hukumomin Kubau, Igabi da Birnin Gwari, a wani yunkuri na dakile ayyukan kungiyoyin ’yan ta’adda da kuma katse hanyoyin samar musu da kayayyaki.
Masanin harkokin tsaro, Zagazola Makama, ne ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a daren Alhamis.
A cewar Makama, sojoji sun kai samame wani wuri da ake kira Dabar Dabo a karamar hukumar Kubau, wanda aka gano cewa ’yan ta’adda na amfani da shi a matsayin maboyarsu. A yayin samamen, an kama wanda ake zargi da jagorantar kungiyar da wasu mambobinsa 2.
Makama ya ce, “The suspects were taken into military custody for further investigation and intelligence gathering.”
A wani samame daban a karamar hukumar Igabi, sojoji sun tare wata mata mai shekaru 50 da ake zargi da safarar harsasai.
An ce jami’an tsaron sun kwato harsasai 300 da aka boye cikin wata jaka da matar ke dauke da ita.
Makama ya ce binciken farko ya nuna cewa matar ta taso ne daga Jihar Zamfara zuwa Lafia, inda ake zargin ta karbi harsasan kafin ta nufi Birnin Gwari domin kai su ga wasu da ake zargi ’yan ta’adda ne a yankin.
Daga bisani a ranar Laraba, sojoji tare da hadin gwiwar ’yan sa-kai na al’umma, sun kama wani mutum da ake zargi da samar da kayan aiki ga ’yan ta’adda a karamar hukumar Birnin Gwari.
Makama ya ce, “A search of the suspect led to the recovery of four communication devices believed to be linked to terrorist activities.”
Ya ce wadanda aka kama da kayayyakin da aka kwato suna hannun sojoji yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike.