Sojoji sun kama wata mata ƴar shekara 50 da ta yi  harsashi 300 

Sojojin rundunar haɗin gwiwa ta Operation FANSAN YAMMA (OPFY) dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso yamma sun kama wata mata mai shekaru 50 da ake zargin tana safarar harsasai ga ‘yan ta’adda a Kaduna. 

A cewar kafar Zagazola Makama, dake wallafa bayanai kan  sha’anin tsaro da yaƙi da  ta’addanci a yankin Tafkin Chadi, an kama matar ne a ranar Laraba, 9 ga Satumba, yayin wani samame a ƙaramar hukumar Igabi ta jihar. 

Makama ya ce an same ta da harsasai 300 da aka ɓoye a cikin jaka. 

Kafar ta Zagazola ta ce binciken farko ya nuna cewa matar ta yi tafiya daga Zamfara zuwa Lafia a jihar Nasarawa, inda a can ne  ta karɓi harsasan don kaiwa ga ‘yan ta’adda da ke aiki a yankin Birnin Gwari na Kaduna. 

Makama ya ce an mika matar tare da harsasan da aka kwato ga rundunar sojoji domin ci gaba da bincike don gano hanyar sadarwarta da kuma wadanda aka nufa da kayan. 

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...