Rundunar Soji Ta Umurci Sojoji Su Kara Tsaurara Yaki Da Ƴan Bindiga A Kebbi



Mukaddashin Kwamandan Brigade ta 1 ta Rundunar Sojin Najeriya, Kanal Joseph Umaru, ya umurci kwamandoji da sojojin da ke karkashin rundunar da su kara tsaurara ayyukan leken asiri da farmaki kan ’yan bindiga da sauran kungiyoyin masu aikata laifuka a Jihar Kebbi.

Umaru ya bayar da umarnin ne yayin rangadin sanin makamar aiki da ya kai ga rundunonin soji daban-daban a jihar tsakanin 8 da 9 ga Satumba, 2026.

Rundunar Sojin Najeriya ta bayyana hakan a wani sako da ta wallafa a shafinta na X ranar Alhamis.

Kwamandan ya bukaci sojojin da su inganta tattara bayanan sirri da musayar bayanai, tare da karfafa hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro, hukumomin kananan hukumomi da sauran masu ruwa da tsaki.

Ya ce irin wannan hadin gwiwa zai taimaka wajen takaita ayyukan masu aikata laifuka tare da hana su samun damar gudanar da ayyukansu cikin sauki a jihar.

Umaru ya kuma umurci kwamandoji da su ci gaba da gudanar da ayyukan hadin gwiwa cikin tsari da kuma daukar matakan dakile barazana tun kafin ta kunno kai. Ya tunatar da sojojin muhimmancin kwarewa, bin dokokin bude wuta da kuma kare fararen hula yayin gudanar da ayyukansu.

Mukaddashin kwamandan ya kuma jaddada bukatar bai wa jin dadin jami’ai, kwarin gwiwa, horaswa da bunkasa kwarewar su muhimmanci.

Ya bukaci kwamandoji su rungumi taken Babban Hafsan Sojin Kasa, wato “Soldiers First”.

Umaru ya ce sojojin da aka jagoranta yadda ya kamata, aka karfafa musu gwiwa tare da samar musu da kayan aiki za su fi samun damar ci gaba da matsin lamba kan masu aikata laifuka da kuma sauke nauyin da aka dora musu.

A yayin rangadin, kwamandan ya duba shirye-shiryen rundunonin da ke karkashin Brigade ta 1 tare da nazarin kalubalen da ke kawo cikas ga ayyukansu.

Rundunonin da ya ziyarta sun hada da Bataliyar Tankokin Yaki ta 223 da ke Zuru, COAS Intervention Battalion III da ke Sakaba da kuma Bataliya ta 1 da ke Birnin Kebbi.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...