
Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Akwa Ibom ta fara bincike kan kisan wani mutum da ba a bayyana sunansa ba, wanda wasu mutane suka kama suka ƙona shi har ya mutu bisa zargin ƙoƙarin satar babur.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7:05 na safe a ƙauyen Ikpe Ikot Akpan, da ke kan hanyar Ikot Ekpene zuwa Uyo.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, DSP Timfon John, ta ce binciken farko ya nuna cewa mutumin ya yi ƙoƙarin satar babur mallakar wani mai suna Idoroenyin Udo.
Ta ce mai babur ɗin ya yi turjiya tare da ɗaga ƙara, lamarin da ya sa wasu mutane suka bi wanda ake zargin har suka kama shi.
“Maimakon su miƙa shi ga ‘yan sanda domin gudanar da bincike yadda ya kamata, wasu daga cikin mutanen sun ɗauki doka a hannunsu, suka lakada wa wanda ake zargin duka sannan suka ƙona shi, lamarin da ya yi sanadin mutuwarsa,” in ji John.
Ta ce bayan samun rahoton lamarin, jami’an ‘yan sanda sun garzaya wurin, inda suka fara bincike.
Rundunar ta ce tana ƙoƙarin gano tare da cafke duk waɗanda suka shiga cikin kisan, kuma za a gurfanar da duk wanda aka samu da hannu a gaban doka.
Kwamishinan ‘Yan Sandan Akwa Ibom, Baba Azare, ya yi Allah-wadai da lamarin tare da jan hankalin jama’a kan illar ɗaukar doka a hannu.
«“Babu wani mutum ko ƙungiya da ke da ikon yanke hukuncin cewa wanda ake zargi yana da laifi ko kuma hukunta shi a wajen tsarin doka.»
«“Dole ne a miƙa mutumin da ake zargi da aikata laifi ga hukumomin da suka dace domin gudanar da bincike da gurfanar da shi,” in ji sanarwar.»
Rundunar ta buƙaci jama’a da su riƙa kai rahoton duk wani abin da suke zargi da aikata laifi ga ‘yan sanda maimakon ɗaukar mataki da kansu.
Ta ce hukuncin ganganci haramun ne, yana da haɗari kuma ba za a amince da shi ba, domin yana iya lalata shaidu, kawo cikas ga bincike tare da jefa rayuwar mutanen da ba su da laifi cikin haɗari.
Rundunar ta ce bincike na ci gaba da ƙoƙarin kama duk waɗanda ke da alaƙa da lamarin.