

Rundunar ‘yan sandan Jihar Benue ta ce ta kama mutane 46 da ake zargi da hannu wajen tare jerin gwanon motocin Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC a lokacin wata ziyarada ya kai jihar ranar Talata.
Kwamishinan ‘yan sanda na Benue, Cletus Nwadiogbu, ne ya sanar da hakan a ranar Laraba yayin da yake jawabi ga ‘yan jaridu a Makurdi, babban birnin jihar.
Nwadiogbu ya ce an sanar da rundunar ‘yan sanda game da ziyarar Obi da misalin ƙarfe 5:30 na yamma a ranar Litinin, inda aka tura jami’an tsaro ciki har da motocin sintiri uku ƙarƙashin jagorancin mataimakin kwamishina.
Ya ce wata ƙungiya ta mutane daga baya ta toshe hanyar Obi, lamarin da ya haifar da tashin hankali wanda zai iya rikidewa zuwa rikici.
Kwamishinan ya ce rundunar ta ƙi amfani da karfi nan take domin kauce wa asarar rayuka da lalata dukiya.
Ya ce daga baya an raka Obi lafiya zuwa filin jirgin sama inda ya bar jihar.
Nwadiogbu ya ce rashin amfani da karfi ba za a fassara shi a matsayin rashin aiki ba, inda ya ƙara da cewa rundunar ta fara bincike ta hanyar leƙen asiri domin gano waɗanda suka shirya lamarin.
“An riga an kama wasu muhimman mutane, kuma ana ci gaba da ƙoƙari don cafke sauran da ke da hannu a lamarin,” in ji shi.
Kwamishinan ya ce rundunar ‘yan sanda ta kasance tsaka-tsaki da ƙwararru, yana mai jaddada cewa kowane ɗan Najeriya na da ‘yancin motsi ba tare da la’akari da jam’iyya, matsayi ko ra’ayi ba.
Ya ce bincike yana ci gaba da gudana kuma duk wanda aka samu da laifi za a gurfanar da shi a gaban alkali domin ya fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.
Ya yi kira ga mazauna jihar da su kwantar da hankalinsu su bar ‘yan sanda su kammala bincike.
“Babu wani mutum ko ƙungiya da ke da ‘yancin hana wani motsi ba bisa ƙa’ida ba,” in ji shi.” A cewar sa.