
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana sauraron ra’ayoyin ’yan Najeriya tare da yin la’akari da damuwarsu kafin gwamnati ta yi gyare-gyare kan manufofinta.
Idris ya bayyana hakan ne a ranar Talata a Abuja, lokacin da wata tawaga daga Cibiyar Nazarin Manufofi da Dabarun Ƙasa (NIPSS), ƙarƙashin jagorancin Darakta-Janar, Farfesa Ayo Omotayo, ta kai wa ma’aikatar ziyara.
Ministan ya ce aikin ma’aikatarsa ba wai yaɗa manufofin gwamnati kawai ba ne, har ma da tattara ra’ayoyin jama’a da mayar da su ga gwamnati domin ta fahimci abin da ’yan ƙasa ke buƙata.
«“Duk lokacin da na zauna da shi, tambayar farko da yake yi ita ce: ‘Me ’yan Najeriya suke cewa?’” inji Idris.»
Ya ce wannan salon yana nuna cewa Shugaban ƙasa yana ganin shugabanci a matsayin tsari mai buƙatar sauraron jama’a da kuma yin gyare-gyare idan hakan ya zama dole.
Idris ya ƙara da cewa Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Ƙasa (NOA) tana da ofisoshi sama da 800 a faɗin ƙasar, abin da ya bai wa gwamnati damar samun ra’ayoyin manoma, ’yan sana’a da sauran jama’a daga matakin ƙasa.
A nasa ɓangaren, Darakta-Janar na NIPSS, Farfesa Ayo Omotayo, ya ce cibiyar ta zaɓi “Orange Economy”, wato tattalin arzikin masana’antun kirkire-kirkire, a matsayin jigon Babban Kwasi na Gudanarwa na 48.
Ya ce binciken zai duba damar da ke cikin wannan fanni da kuma yadda zai taimaka wajen samar da ayyukan yi da kuma cimma burin gina tattalin arzikin Najeriya mai darajar dala tiriliyan ɗaya.