Sojoji Sun Ceto Fararen Hula 12 Daga Hannun ’Yan Ta’adda A Zamfara

Muhammadu SabiuHausa20 minutes ago



Rundunar Operation Fansan Yamma ta ce dakarunta sun ceto fararen hula 12 daga hannun ’yan ta’adda a wasu samame daban-daban da suka gudanar a ƙananan hukumomin Kaura Namoda da Tsafe na Jihar Zamfara.

Jami’in yaɗa labarai na rundunar, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya ce an gudanar da ayyukan ne a ranar Litinin.

Ya bayyana cewa a Kaura Namoda, dakarun sun mayar da martani kan kiran neman agaji bayan ’yan ta’adda sun kai hari wani gida da ke Tsohon Tasha, inda suka yi musayar wuta da su.

A cewarsa, ’yan ta’addan sun tsere ta wani kogi da ke kusa, bayan sun bar wasu mutane shida da suka yi garkuwa da su. Sojojin sun ceto mutanen tare da kai su wuri mai tsaro, daga bisani aka haɗa su da iyalansu.

A wani samame da aka gudanar a Tsafe, sojoji sun gano ’yan ta’addan da ke ƙoƙarin tare wata motar Sharon a ƙauyen Kwanoni.

Danja ya ce dakarun sun yi gaggawar isa wurin tare da tunkarar ’yan ta’addan, lamarin da ya tilasta musu tserewa zuwa cikin daji tare da barin fararen hula shida da suka kama.

Rundunar ta ce ayyukan sun nuna ƙudurin Operation Fansan Yamma na kare rayuka da dukiyoyi tare da dakile ayyukan ’yan ta’adda a yankin da take gudanar da ayyukanta.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...