
Ɗan takarar gwamnan Jihar Benue na jam’iyyar PDP, Chief Michael Aondoakaa, ya ce babu wata doka da ta bai wa gwamna damar yin shekaru takwas kai tsaye a kan mulki.
Aondoakaa, wanda ya taɓa zama Attorney-General kuma Ministan Shari’a na Ƙasa, ya ce zaɓen gwamna na 2027 zai ba al’ummar Benue damar tantance ko Gwamna Hyacinth Alia ya cancanci samun wa’adin mulki na biyu.
Ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin da yake magana da manema labarai a Makurdi, inda ya nuna kwarin gwiwar cewa zai iya kayar da gwamnan mai ci.
A cewarsa, Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya bai wa gwamna wa’adin farko na shekaru huɗu, yayin da samun wasu shekaru huɗun ya dogara ne da zaɓin masu kaɗa ƙuri’a.
“Doka ba ta ba gwamna shekaru takwas ba. Ta ba shi shekaru huɗu. Sauran shekaru huɗun su ne al’umma ke ba ka,” inji shi.»
Aondoakaa ya danganta kwarin gwiwarsa na kayar da gwamnatin Alia da abin da ya bayyana a matsayin rashin kusancin gwamnan da jama’a, ƙara tabarbarewar tsaro da kuma rashin daidaito wajen rarraba ayyukan ci gaba a faɗin jihar.
Ya ce damar samun shugabanni cikin sauƙi na daga cikin abubuwan da suka taimaka wa wasu gwamnonin baya wajen samun wa’adin mulki na biyu.
Ya kuma yi kira ga masu riƙe da mukaman siyasa da su kasance kusa da al’ummar da suke wakilta, yana mai cewa zaɓen 2027 zai kasance hannun al’ummar Benue wajen tantance ayyukan gwamnatin yanzu da kuma yanke shawarar ko za su sake ba ta dama.