
Jam’iyyun siyasa 19 a Jihar Kogi sun sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya domin tabbatar da gudanar da zaɓukan 2027 cikin lumana.
An sanya hannu kan yarjejeniyar ne a ranar Talata yayin wani taro tsakanin Kwamitin Tuntuɓa Kan Tsaron Zaɓe da jam’iyyun siyasa, wanda aka gudanar a hedikwatar rundunar ’yan sandan jihar da ke Lokoja.
Daga cikin jam’iyyun da suka halarci taron akwai APC, ADC, PDP, SDP, NDC, PRP da Action Alliance (AA), da wasu jam’iyyu.
A ƙarƙashin yarjejeniyar, jam’iyyun da ’yan takararsu sun amince su gudanar da kamfen bisa manufofi, shirye-shirye da manufofin jam’iyyunsu, tare da mayar da hankali kan abubuwan da suka shafi ci gaban al’ummar Kogi.
Sun kuma yi alƙawarin guje wa kalaman ƙiyayya, rikicin kabilanci ko addini, hare-haren kai tsaye kan abokan hamayya, kalaman tayar da hankali da kuma tunzura jama’a.
Jam’iyyun sun ƙi amincewa da amfani da mutane ko ƙungiyoyi wajen tada hankalin jama’a, tsoratarwa, barazana ko kawo cikas ga harkokin siyasa. Sun kuma yi alƙawarin tabbatar da cewa magoya bayansu sun gudanar da ayyukansu cikin lumana.
Haka kuma, sun amince da mutunta ’yancin Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) da sauran hukumomin da ke da alhakin gudanar da tabbatar da tsaron zaɓe.
Yarjejeniyar ta kuma haramta yaɗa bayanan ƙarya da gangan, saƙonnin tunzura jama’a da duk wani abu da ka iya haifar da tashin hankali ko rage amincewar jama’a ga tsarin zaɓe.
Jam’iyyun sun ce duk wanda bai gamsu da sakamakon zaɓe ba ya kamata ya bi hanyoyin doka wajen neman haƙƙinsa, maimakon komawa ga tashin hankali.
Taron ya samu halartar jami’an ’yan sanda, INEC, sauran hukumomin tsaro, ƙungiyoyin fararen hula da masu sa ido kan zaɓe, da kuma wakilan hukumomin addini.