

‘Yan bindiga sun kashe mambobi uku na Hukumar Tsaron Bijilante ta jihar Kaduna (KADVS) tare da yin garkuwa da ɗan’uwan ɗan majalisa a ƙaramar hukumar Kubau ta jihar.
A cewar kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN, jami’in hulɗa da jama’a na KADVS, Yunusa Ibrahim, shi ne ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Talata.
Ibrahim ya ce maharan sun kashe jami’an tsaron ne a yankin Zaria-Pambegua na jihar kafin su yi garkuwa da Sanusi, ƙanin Shehu Pambegua, ɗan majalisar jiha da ke wakiltar mazabar Kubau a majalisar dokokin jihar Kaduna.
Ya ce an yi garkuwar ne da Sanusi da misalin ƙarfe 10 na daren ranar Litinin lokacin da wasu da ake zargin ‘yan fashi ne suka shigo garin a mota suka kuma kutsa kai gidan Sanusi.
Ibrahim ya bayyana sunayen waɗanda suka rasu da suka haɗa da Dallami Dantani, mataimakin kwamandan KADVS a Kubau LGA, Abdullahi Hamisu, da Zakariyya Musa.
Ya ce jami’an tsaron bijilanten suna gudanar da binciken tsaro na yau da kullum ne lokacin da suka yi ƙoƙarin tsayar da wata jar motar Volkswagen, amma direban ya ƙi tsayawa, lamarin da ya sa suka bi motar da motar sintiri domin gano mutanen da ke ciki da kuma manufar tafiyarsu.
Ya ce Dantani ya rasa ransa yayin bin motar, sannan daga baya maharan suka juya zuwa ofishin KADVS inda suka harbe Hamisu da Musa har lahira kafin su tsere zuwa Zaria.
Kwamandan KADVS na Kaduna, Ali Audu, ya bayyana mutuwar a matsayin “rashi mai raɗaɗi” ga hukumar, tare da yin ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasu.
Audu ya ce an ƙara tsaurara sa ido a Pambegua da makotan garuruwa, kuma hukumomin tsaro suna aiki don ceto wanda aka yi garkuwa da shi.