Harin sojan sama ya halaka yan bindiga da dama a jihar Zamfara

Wasu ‘yan ta’adda sun halaka a yankin Yankuzo, dake karamar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara, bayan rundunar sojin sama ta kai hare-hare a ranar Litinin da yamma.

Rahotanni sun  nuna cewa rundunar tsaro karkashin ta  Operation Fansan Yanma ce ta kashe ƴan ta’addan a wani farmaki da ta kai ranar Litinin, kamar yadda jaridar Zagazola Makama ta bayyana.

Wasu majiyoyi daga yankin sun ce jiragen yaki guda biyar ne suka shiga wannan aiki tare da kai hare-hare kan mutanen da ake zargin ‘yan ta’adda ne da suka shiga garin.

A cewar rahotanni ean kashe da dama daga cikin ‘yan ta’addan, duk da cewa ba a tabbatar da adadin wadanda suka mutu ba a halin yanzu.

Majiyoyi sun ce daga cikin wadanda aka kashe akwai wani da ake kira Isiya Gurgu, wanda ake ganin na hannun dama ne ga wani shahararren shugaban ‘yan ta’adda da ake kira Musa Commander, wanda ake danganta shi da cibiyar Ado Aleru.

An kuma bayyana cewa Musa Commander yana da alaka da wasu al’ummomi da ‘yan ta’adda ke iko da su, ciki har da Tsamiya da wasu kauyuka a yankin.

Majiyoyin sun kara da cewa jami’an tsaro sun yi taka-tsantsan wajen gudanar da aikin domin kauce wa kashe fararen hula, inda suka fi mayar da hankali kan mutanen da aka gani dauke da makamai ko kuma sanye da kayan soja.

An kuma ce wasu daga cikin ‘yan ta’addan sun jikkata a hare-haren.

Yankin Yankuzo dai ana daukarsa a matsayin cibiyar ‘yan ta’adda da ke da alaka da cibiyar Ado Aleru, inda mazauna yankin ke fuskantar barazana daga wadannan kungiyoyi. 

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...