An Cafke Mutane 4 Kan Zargin Yanke Yatsa Don Neman Naira Miliyan 80 A Wajen Boka

Muhammadu SabiuHausa12 minutes ago



Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta cafke mutane 4 bisa zargin hannu a wani lamari da ya shafi wani matashi da ake zargi da yanke yatsarsa domin kai wa wani boka, bayan an yi masa alkawarin samun Naira miliyan 80.

Kakakin rundunar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa binciken ‘yan sandan ya gano cewa an yi wa matashin alkawarin samun makudan kuɗi, wanda daga bisani ya ce bai samu kuɗin da aka yi masa alkawari ba.

Kiyawa ya shaida wa manema labarai cewa binciken da rundunar ta gudanar ya kai ga gano wasu mutane da ake zargi da hannu a lamarin, tare da cafke su.

A yayin binciken, matashin da ake zargi da kuma bokan sun yi bayanai kan abin da ya faru, inda kowannensu ya bayyana nasa ɓangaren dangane da zargin.

Rundunar ‘yan sandan ta ce bincike na ci gaba da gudana domin gano cikakken abin da ya faru da kuma tabbatar da rawar da waɗanda aka cafke suka taka a lamarin.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...