
Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta kama mutane 2 da ake zargi da hannu a kisan fitaccen mai sharhin siyasa, Ibrahim Khalil Danshagamu, wanda aka kai wa hari a gidansa da ke Gaida Quarters, Ƙaramar Hukumar Kumbotso.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:30 na dare ranar Litinin, bayan rundunar ta samu kiran gaggawa daga kwamandan kungiyar ‘yan banga ta Gaida, inda ya sanar da cewa wasu ‘yan daba sun shiga gidan mamacin da ƙarfi tare da kai masa hari da makamai masu kaifi.
Sanarwar da Kakakin Rundunar, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar a madadin Kwamishinan ‘Yan Sanda, CP Ibrahim Adamu Bakori, ta ce jami’an sashen ‘yan sanda na Kumbotso sun isa wurin cikin gaggawa.
An garzaya da Danshagamu zuwa Asibitin Kwararru na Murtala Mohammed da ke Kano, inda likita ya tabbatar da cewa ya mutu bayan isar da shi asibitin.
Kakakin rundunar ya ce kama mutanen 2 ya biyo bayan wani samame da aka gudanar bisa bayanan sirri, tare da haɗin gwiwar jami’an sashen Kumbotso, rundunonin musamman da wasu masu ruwa da tsaki a cikin al’umma.
Ya ce waɗanda ake zargin suna hannun ‘yan sanda kuma ana yi musu tambayoyi, yayin da ake ƙoƙarin cafke wasu da ka iya kasancewa da hannu a kisan.
Binciken kuma ya haɗa da tattara bayanan mutane masu alaƙa da lamarin da kuma gudanar da binciken ƙwararru domin gano yadda kisan ya faru da kuma dalilinsa.
Tsohon Gwamnan Kano kuma ɗan siyasar adawa, Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi Allah-wadai da kisan, yana mai cewa an samu gawar Danshagamu cikin jini a gidansa.
Ƙungiyar Amnesty International Nigeria ma ta yi Allah-wadai da lamarin tare da buƙatar gudanar da cikakken bincike.
«“A tsarin dimokuraɗiyya, ana karɓar masu bayyana ra’ayinsu da masu suka, ana sauraren su, ba a kashe su ba,” in ji ƙungiyar.»
Kwankwaso ya yi kira ga gwamnatin Jihar Kano da ta kafa kwamitin bincike domin gano waɗanda ke da hannu a kisan tare da tabbatar da an gurfanar da su a gaban shari’a.
Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar ya jajanta wa iyalan mamacin tare da tabbatar wa jama’a cewa rundunar za ta bi lamarin har zuwa ƙarshe.
«“Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen cika aikinta na kare rayuka da dukiyoyi. Muna tabbatar wa al’ummar Kano cewa za a bi diddigin lamarin har sai an tabbatar da adalci,” in ji Bakori.»
Rundunar ta ce za a gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu bayan kammala bincike, yayin da aka ƙara yawan sintiri da ayyukan tattara bayanan sirri a Gaida da yankunan da ke makwabtaka da shi domin tabbatar da zaman lafiya.