
Dakarun sojan Najeriya bataliya ta 3 sun samu nasarar dakile wani farmaki da ake zargin mayakan ƙungiyar ISWAP da kaiwa a karamar hukumar Ngala dake jihar Borno.
Kafar yada labarai ta Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi ta ruwaito majiyar jami’an tsaro na cewa yan ta’addar sun ƙaddamar da farmakin ne da ƙarfe 02:45 na daren ranar Juma’a inda suka farka dakarun sojan lokaci guda ta bangarorin Wurje, Manawaji da Kinuba
A cewar majiyoyi sojoji sun mayar da martani da manyan makamai da suka fi na yan ta’addan kana suka samu karin taimako daga hedkwatar bataliyar da kuma bindigogin atilare abun da ya tilastawa yan ta’addan ja da baya.
Biyo bayan arangamar yan ta’addar sun ja da baya tare da fantsama cikin daji.
Majiyar ta kara da cewa da misalin karfe 05:45 na asuba dakarun suka bi sawun hanyar da yan ta’addan su ka bi su ka tsere inda suka gano bama bama guda uku na bindigar roka da kuma na’urar fitilar tocilan guda biyu.
Sai dai kuma Soja guda ne ya jikkata a yayin arangamar kuma tuni aka ɗauke shi ya zuwa bada agajin gaggawa na bataliyar domin karɓar magani.

