
Wakilan jam’iyyu da basu gaza 20 ba ne aka kama da aikata laifin sayen kuri’a ranar Asabar a wurin zaɓen ƙananan hukumomi 6 dake faɗin birnin tarayya.
Jami’an hukumar EFCC dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati ne su ka kama mutanen a ƙananan hukumomin Abaji, Kuje, Kwali da kuma Gwagwalada a yayin zaɓen da ya gudana.
Tuni dai hukumar zaɓe ta ƙasa mai zaman kanta INEC ta sanar da cewa jam’iyar APC ta lashe kujeru biyar a cikin ƙananan hukumomin 6 c yayin da PDP ta tashi da kujera guda.
Mai magana da yawun hukumar EFCC Dele Oyewale ya ce biyu daga cikin mutanen an kama su ne a Abaji, 9 a Gwagwalada huɗu a Kuje a yayin da sauran huɗun aka kama su a Kwali.
Oyewale ya bayyana cewa an kama mutanen da kuɗaɗe masu yawa da su ka kai sama da naira miliyan 30 a dai-dai lokacin da suke kokarin sayen kuri’a a ya yin da ake cigaba da gudanar da bincike.

