Ma’aikatan lafiya sun dakatar da yajin aikin da su ke

Ƙungiyar JOHESU gamayyar ma’aikatan kiwon  lafiya ta dakatar da yajin aikin da suka shafe kwanaki 84 suna yi a faɗin biyo  bayan wata yarjejeniya da su ka cimma da gwamnatin tarayya kan albashi da kuma walwalarsu.

An ɗauki matakin janye yakin aikin ne a ƙarshen taron shugabannin gudanarwar kungiyar da aka gudanar ranar Juma’a a Abuja.

Kungiyar ta ce an kira taron ne domin sake duba sakamakon da aka samu na tattaunawar sulhu tsakanin ɓangaren gwamnatin tarayya da kuma JOHESU wanda aka yi ranar Alhamis a hedkwatar ma’aikatar kwadago ta tarayya.

A wata sanarwa da aka fitar bayan taron kungiyar ta ce an dakatar da yakin aikin domin bawa gwamnati damar aiwatar da yarjejeniyar aka cimma.

More from this stream

Recomended