
Shugaban jam’iyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje ya sauka daga kan mukaminsa na shugabancin jam’iyar.
Ganduje wanda ya yi mulkin jihar Kano daga shekarar 2015 ya zuwa 2023 ya sanar da yin murabus nan take ba tare da bata lokaci ba.
Babu wani cikakken bayani kan musabbabin yin murabus din nasa sai dai Ganduje ya fadi cewa ya yi murabus domin ya kula da lafiyarsa a cikin takardar murabus din ya mikawa jam’iyar.
Sai dai wasu majiyoyi dake cikin jam’iyar ta APC sun bayyana cewa murabus din nasa na da alaka da rikicin da ya yi tsamari a cikin jam’iyar ta APC.