Tinubu ya kaddamar da ginin ofishin hukumar zabe ta INEC a Abuja

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya kaddamar da aikin ginin ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta INEC a Abuja.

Da yake magana a wurin bikin aza harsashin tubalin ginin a ranar Talata, Mahmoud Yakubu shugaban hukumar INEC ya yabawa Tinubu da ya samu damar halartar bikin.

Yakubu ya ce hukumar ta shafe tsawon lokaci tana fama da cinkoso a ginin hedkwatar hukumar na yanzu wacce a kaddamar da ita a shekarar 1997.

Ya ce tun da farko an tsara ginin ya zama karami amma amma yanzu an yi masa yawa saboda karuwar yawan ayyukan da hukumar take yi .

Ya ce saboda rashin wadata wuri ya sa tilas hukumar ta karbi hayar  karin wasu gine-gine guda biyu a unguwar Wuse Zone II domin ajiye ma’aikata da kuma sauran ayyukan yau da kullum a ciki hara ganawa da masu ruwa da tsaki kan harkokin zabe.

Hukumar birnin tarayya Abuja a karkashin jagorancin ministan birnin,  Nyesom Wike ce ta dauki nauyin ginin sabon ofishin.

More from this stream

Recomended