Rahotanni daga jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya sun ce mayaƙan ISWAP sun kashe aƙalla mutum 13 a ƙauyuka da dama na jihar Borno.
An kai hare-haren ne a ƙauyuka huɗu, cikin kwanaki biyu.
Wasu mazauna ƙauyukan sun shaida wa wasu jaridun Najeriya cewa mayaƙan sun kuma sace mutane da dama.