Ćłan sanda sun sake rufe majalisar dokokin Plateau, a Jos babban birnin jihar.
Wannan lamarin dai ya haifar da zaman zullumi da neman tayar da tarzoma a harabar a yau Laraba.
Rahotanni sun nuna cewa wani dan majalisar, Gwottson Fom, daga mazabar Jos ta Kudu ya tabbatar da faruwar lamarin.
Dan majalisar wanda ya soki abin da Ć´an sandan suka yi, ya ce matakin ya hana mambobin zamansu na yau Laraba.