Ƴan sanda sun rufe majalisar dokokin Filato

Ƴan sanda sun sake rufe majalisar dokokin Plateau, a Jos babban birnin jihar.

Wannan lamarin dai ya haifar da zaman zullumi da neman tayar da tarzoma a harabar a yau Laraba.

Rahotanni sun nuna cewa wani dan majalisar, Gwottson Fom, daga mazabar Jos ta Kudu ya tabbatar da faruwar lamarin.

Dan majalisar wanda ya soki abin da ƴan sandan suka yi, ya ce matakin ya hana mambobin zamansu na yau Laraba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]