An ba wa sojoji tukwici saboda ƙin karɓar cin hanci daga wasu ɓarayin shanu

Rundunar soji ta musamman mai kula da wanzar da zaman lafiya a jihar Filato ta bayyana cewa, a ranar Talata, ta bayar da tukwici ga wasu jami’an ‘Operation Safe Haven’ guda takwas bisa kin karbar cin hancin N1.5m daga wasu da ake zargin barayin shanu ne a jihar.

Kakakin rundunar, Kaftin Oya James, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Talata, ya ce jami’an 8 da aka tura a sashin OPSH 4, sun kama wasu barayin shanu 30 a shingen binciken Bisichi da ke karamar hukumar Barkin Ladi ta jihar.

A cewarsa, an yi awon gaba da shanun wani Shehu Umar ne a garin Mangu kuma ana ƙoƙarin kai su zuwa wani wuri da ba a bayyana ba.

Har sai da dakarun rundunar da ke aikin kawo lumana suka tare su.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]