An ba wa sojoji tukwici saboda ƙin karɓar cin hanci daga wasu ɓarayin shanu

Rundunar soji ta musamman mai kula da wanzar da zaman lafiya a jihar Filato ta bayyana cewa, a ranar Talata, ta bayar da tukwici ga wasu jami’an ‘Operation Safe Haven’ guda takwas bisa kin karbar cin hancin N1.5m daga wasu da ake zargin barayin shanu ne a jihar.

Kakakin rundunar, Kaftin Oya James, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Talata, ya ce jami’an 8 da aka tura a sashin OPSH 4, sun kama wasu barayin shanu 30 a shingen binciken Bisichi da ke karamar hukumar Barkin Ladi ta jihar.

A cewarsa, an yi awon gaba da shanun wani Shehu Umar ne a garin Mangu kuma ana ƙoƙarin kai su zuwa wani wuri da ba a bayyana ba.

Har sai da dakarun rundunar da ke aikin kawo lumana suka tare su.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...