‘Ƴan sanda sun cafke ‘yan fashi hudu a Bauchi

Rundunar ƴan sandan jihar Bauchi ta kama wasu mutane hudu da ake zarginsu da fashi da makami da kuma wasu yan sara suka su 60 a fadin jihar.

Anyi holin munanen da ake zargi ne a hedkwatar rundunar dake Bauchi.

A cewar mai magana da yawun rundunar yansandan jihar,Kamal Datti Abubakar an samu wannam. nasara ne sakamakon cigaba da jajircewa da kwamishinan ƴansandan jihar,Habu Sani Ahmadu yake na raba jihar da bata gari.

An kama yan fashin ne a yankin Kofar Wambai dake cikin birnin jihar biyo bayan samun bayanan sirri da rundunar ta yi.

Mutanen sunyi fashin wata mota kirar Jeep daga hannun wata mata akan hanyar Abuja zuwa Jos.

Yan fashin da suka fada hannun jami’an tsaron sun hada da Audu Daniel mai shekaru 29 dan asalin jihar Benue da kuma John Samuel dan jihar Imo.

Datti ya kara da cewa a wani samame na daban rundunar ta samu nasarar kama yan Sara-Suka inda ta same su da adduna 11, wukake biyu da kuma kwalin kwaya 8.

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...