Kwamitin majalisar wakilai kan harkokin sufurin jiragen sama ya bukaci gwamnati da ta dakatar da kafa kamfanin Najeriya Air.
Kwamitin ya cimma wannan matsaya ne a ranar Talata bayan wani bincike da aka gudanar kan kamfanin jirgin.
Idan dai za a iya tunawa tsohon ministan sufurin jiragen sama Hadi Sirika ya kaddamar da kamfanin jirgin ne jim kadan kafin ya bar aiki.
Sai dai a zaman da kwamitin ya gudanar ya gano cewa har yanzu kamfanin jirgin bai samu amincewar da ya kamata ba kafin kaddamar da shi.