Ƴan majalisa sun nemi a dakatar da Nigeria Air

Kwamitin majalisar wakilai kan harkokin sufurin jiragen sama ya bukaci gwamnati da ta dakatar da kafa kamfanin Najeriya Air.

Kwamitin ya cimma wannan matsaya ne a ranar Talata bayan wani bincike da aka gudanar kan kamfanin jirgin.

Idan dai za a iya tunawa tsohon ministan sufurin jiragen sama Hadi Sirika ya kaddamar da kamfanin jirgin ne jim kadan kafin ya bar aiki.

Sai dai a zaman da kwamitin ya gudanar ya gano cewa har yanzu kamfanin jirgin bai samu amincewar da ya kamata ba kafin kaddamar da shi.

More News

Ɗalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...