Kotu ta bayar da belin Hadi Sirika da ƴarsa

Wata babbar kotun tarayya dake Abuja ta bayar da belin tsohon ministan harkokin sufurin jiragen sama, Hadi Sirika da kuma wasu mutane uku kan kuɗi naira miliyan 100 kowannen su.

Hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati ce ita gurfanar da Sirika tare da ƴarsa Fatima a gaban Mai Shari’a Sylvanus Oriji na babbar kotun birnin tarayya Abuja dake Maitama a ranar Alhamis.

Ƙarin waɗanda aka gurfanar sun haɗa da Jalal Hamma tare da wani kamfani Al-Duraq Investment Ltd inda ake tuhumarsu da wawashe dukiyar al’umma har naira biliyan biyu da miliyan ɗari bakwai.

A cewar takardun ƙarar Sirika ya yi amfani da matsayinsa na ministan Sufurin Jiragen Sama inda ya riƙa bawa kansa kwangila, sirikinsa da kuma makunsantarsa.

A yayin da kotun ke sanar da hukuncin kotun ta ce dole kuma su kawo mutane biyu da za su tsaya musu.

More News

An sanar da zaman makoki na kwana biyar saboda mutuwar shugaban kasa a Iran

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya sanar da zaman makoki na kwanaki biyar saboda rasuwar shugaban kasar Ibrahim Raisi...

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...