Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika, ya kare tarihin tattalin arzikin gwamnatin tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, inda ya musanta zargin cewa gwamnatin ta bar Najeriya cikin mawuyacin hali.
Da yake magana a wata hira da gidan talabijin na Arise Television, Sirika ya ce gwamnatin Buhari ta bar ƙasar cikin kyakkyawan yanayin tattalin arziki da zamantakewa.
Sirika ya kuma ƙi yin suka ga gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana cewa ba zai yi wa manufofin gwamnatin da ba ya cikinta sharhi ba.
Ya ƙara da cewa manufofin gwamnatocin Buhari da Tinubu sun samo asali ne daga jam’iyyar APC, saboda haka ba ya ganin ana aiwatar da su ne da nufin cutar da ƙasar.
Hadi Sirika Ya Ba Da Kariya Wa Matakan Tattalin Arzikin Tsohon Shugaba Buhari

